Jihohi 20 sun Gaza Cika Ka'idojin Samun Tallafin Biliyan 45.7 -UBEC

top-news

Sakataren Hukumar Ilimi na Kasa (UBEC), Dokta Hamid Bobboyi, ya bayyana cewa sama da Naira biliyan 45.7 na tallafin da aka ware wa jihohi don aiwatar da shirin ilimi na UBEC daga shekarar 2020 zuwa 2023, bai samu karbuwa daga yawancin jihohi ba.

Ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin da ya karbi bakuncin membobin kwamitin majalisar wakilai na ilimi na asali da ayyuka yayin ziyarar sa ido zuwa hukumar a Abuja. Bobboyi ya bayyana cewa jihohi 16 kacal suka karbi tallafin na 2023, daga cikin 36, wanda ya kai kashi 41 cikin dari na Naira biliyan 51.6 da aka ware.

Ya bayyana cewa Naira biliyan 51.6 din da gwamnatin tarayya ta ware a matsayin tallafi ga jihohi a shekarar 2023, amma Naira biliyan 21 kacal aka karba daga jihohi 16 har zuwa ranar 30 ga Yuni.

Ya bayyana jihohin 16 a matsayin Benue, Borno, Cross River, Delta, Enugu, Jigawa, Kano, Kwara, Nasarawa, Niger, Ondo, Osun, Rivers, Sokoto, Taraba da Zamfara.

Ya ce daya daga cikin matsalolin da hukumar ke fuskanta shi ne rashin jajircewar jihohi wajen karbar tallafin UBEC a kan lokaci.

Bobboyi ya bayyana cewa kokarin samar da ingantaccen ilimi na asali da magance matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta a Najeriya yana bukatar hadin kai daga dukkanin masu ruwa da tsaki, ciki har da majalisar dokoki ta kasa.

Ya nuna damuwa cewa wasu gwamnatocin jihohi na kasa rashin jajircewa ga al'amuran siyasa wajen inganta ilimi na asali, yana mai cewa hakan ya kara tabarbarewar matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta a kasar.

Shugaban kwamitin majalisar wakilai na ilimi na asali da ayyuka, Mark Bako Useni, ya nuna damuwa cewa dokar UBEC ta kusan shekaru 20 da ta wuce ba ta dace ba wajen magance matsalolin ilimi na asali a Najeriya, don haka akwai bukatar a gyara dokar cikin gaggawa.

NNPC Advert